siyasa:- APC Ce Ta Dauki Nauyin Wasu Gidajen Jaridu Domin Batama Kwankwaso Suna Inji Yan Kwankwasiyya
APC Ce Ta Dauki Nauyin Wasu Gidajen Jaridu Domin Batama Kwankwaso Suna Inji Yan Kwankwasiyya.. Wani Labari Da wata Jarida Ta wallafa A Shafinta Kamar Haka…. Kwankwaso Ya Fice Daga Zauren Taron Jam’iyar PDP Tsohon gwamnan jihar Kano, kuma Sanata mai wakiltar jihar ta tsakiya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya fice daga zauren taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar a PDP. Wannan ya biyo bayan fatali da masu ruwa da tsaki na jam’iya a jihar suka yi da yarjejeniyar da Kwankwaso ya ce sun yi da shuagabannin jam’iyar ta kasa da sharadin cewa muddin ya fice daga jam’iyar APC zuwa PDP za a ba shi damar ya tsayar da dan takarar gwamna a jihar tare da ba shi tikitin tsayawa takara shugabancin kasar nan, yarjejeniyar da ya ce sun rattaba hannu. Majiyarmu ta ruwaito cewa masu ruwa da tsaki na jam’iyar a jihar sun sa kafa suka watsar da batun, inda suka tabbatar wa dan siyarar cewa su ba za su yi amfani da wannan batun ba in har ma akwai yarjejeniyar. Cewar yan Kwankwasiyya Wannan Zance Karyace Bugu Da Karima Shi Jagoran Na Kwankwasiyya Yau Kusan Kwana Uku Kenan Yana Tsakanin Jihohin Rivers Cross Rivers Da Uyo Yana Ziyararsa Ta Habbaka Siyasarsa….. #Mikiya
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!