siyasa:- Ni Da Buhari Danjuma Ne Da Danjummai -Cewar Gwamna Ganduje
Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR ya ja Hankalin ‘Yan Jam’iyyar APC Na Jihar Kano akan taba muhibbar duk wani wanda yake Tafiyar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a Jihar Kano.
Gwamna ya bayyana haka ne yau a wajen Bikin Ranar Matasa ta Duniya wanda aka Gabatar a dakin Wasa Na Sani Abacha dake Kofar Mata inda yace Koda Shugaban Kasa Muhammadu Buhari mutum yake kauna Amma baya kaunarsa to kada a zage shi domin da shi da Muhammadu Buhari Danjuma ne da Danjimmai don haka kar a zage shi.
Ya ja Hankalin Matasa akan wasu da ya ji suna zagin masu mukamai a Gwamnatin Tarayya daga jihar Kano inda ya umarce su da su daina.
SSA Social Media II,Kano Abubakar Aminu Ibrahim
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!