labarai:- Shugaban kasa Shugaba Buhari ya kai ziyara jihar Katsina
Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya kai ziyarar jaje jihar Katsina safiyar ranar juma'a 29 ga watan Yuni.
Shugaban ya kai ziyarar ne domin jajanta ma gwamnati da al'ummar jihar bisa ruwan sama da ta fado kwanan baya wanda yayi sanadin asara dukiyoyi. Kamar yadda rahotannin suka bayyana shugaban, zai kuma gana da shugaban kasar Togo, Faure Eyadema, a nan gidan gwamnatin jihar Katsina.
Shugabannin zasu tattauna kan muhimman batutuwa wanda zai inganta alakar kasashen su musamman ta hanyar kasuwanci. Rahotanni sun kuma bayyana cewa shugaban zai garzaya kasar Mauritaniya ranar asabar 30 ga wata.
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!