Arba'una hadis:- hadisi na goma sha takwas 18
ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﺜﺎﻣﻦ ﻋﺸﺮ: ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺫﺭ ﺟﻨﺪﺏ ﺑﻦ ﺟﻨﺎﺩﺓ، ﻭﺃﺑﻲ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻣﻌﺎﺫ ﺑﻦ ﺟﺒﻞ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻤﺎ ﻋﻦ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ: ﺍﺗﻖ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﻴﺜﻤﺎ ﻛﻨﺖ، ﻭﺃﺗﺒﻊ ﺍﻟﺴﻴﺌﺔ ﺍﻟﺤﺴﻨﺔ ﺗﻤﺤﻬﺎ، ﻭﺧﺎﻟﻖ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺑﺨﻠﻖ ﺣﺴﻦ«، ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻭﻗﺎﻝ: ﺣﺪﻳﺚ ﺣﺴﻦ، ﻭﻓﻲ ﺑﻌﺾ ﺍﻟﻨﺴﺦ: ﺣﺴﻦ ﺻﺤﻴﺢ. HADISI NA GOMA SHA TAKWAS: An ruwaito daga Abu Zarri; wato Jundubu xan Junadata, da Abu Abdurrahman; wato Mu’azu xan Jabal (R.A), yace: Manzon Allah (s.a.w) yace: “Ka kiyaye dokokin Allah, a duk inda kake, kuma ka biyo da kyakkyawan aiki bayan mummmuna; sai ya shafe shi, kuma ka xabi’anci mutane da kyakkywar xabi’a”. Tirmizi [1987] ya ruwaito shi. Yace: hadisi ne mai kyau (hasan). A wani bugun kuma: mai kyau ingantacce (hasanun sahihun).
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!